IQNA

Gabar Da Malaman Saudiyyah Ke Yi Da Musulunci Ta Fi Ta Yahudawa Muni

17:58 - August 13, 2015
Lambar Labari: 3342847
Bangaren kasa da kasa, wani marubuci a kasar hadaddiyar daular larabawa yay i kakakusar suka dangane da yadda malaman wahabiyawa suke wuce gona da iri wajen gaba da addini.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Hamrain News cewa, Hamad Almazrui wani marubucin kasar hadaddiyar daular larabawa kuma na hannun damar yarima mai jiran gado na Abu Dhabi, ya soki lamirin malaman wahabiyawa masu bata sunan muslunci.

Shi dai wannan marubuci a kasar hadaddiyar daular larabawa ya yi wanann rubutu ne na kakakusar suka dangane da yadda malaman wahabiyawa suke wuce gona da iri wajen gaba da addini bayan kai garin Saudiyyah.

Almazrui y ace malaman wahabiya da malaman yahudawa duk makiya addinin muslunci ne, kuma duk abin daya suke yi domin rusa addinin muslunci, inda ya bayar da misali da wasu fitattun malaman wahabiyawa kamar Al-uraifi da kuma Al’audah, wadanda suka shahara wajen cutar da addini.

Ya ce irin wadannan malamai sun shahara a duniyar musulmi wajen bata sunan muslunci, tare da bakanta shia  fuskar duniya, da suka da su Al’Uraifi, Al’audah, Alkarni, Alqardawi, Alsuwaidan, Aludha da sauransu, wadanda ya ce babu wanda ya kais u gaba da muslunci.

Wannan dai ba shi ne karon farko da Almazrui yake sukar malaman wahabiyawa ba.

3341812

Abubuwan Da Ya Shafa: uae
captcha