Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga bangaren yada labarai na cibiyar yada al’adun muslucni cewa, jaridar Ghana Times ta buga sakon kagoran juyin juya halin muslucni kan taron arbaeen da aka gudanar a wannan shekara.
A cikin rahoton nata, jaridar ta kawo ganawar da ta gudana tsakanin jagoran juyin juya halin na kasar Iran Ayatollah Sayyid Ali Khamenei da kuma wasu tawagogin Irakawa da suka ziyarce a lokacin tafiya taron ziyarar arbaeen, inda ya yaba da kokarin da dukkanin bangarori suke domin ganin wannan taro ya gudana a cikin nasara.